Me yake kawo tashin zuciya bayan cin abinci



DR SHUAIBU MB
DAGA ZAUREN KIWON LAFIYA🚑🚑
 TAMBAYA:    
Me yake kawo tashin zuciya bayan cin abinci❓

🤔 Tashin zuciya ko amai su karan kansu ba cututtuka bane amma alamomi ne na wasu cututtukan misali kamar laulayi ko morning sickness bawai ga mai ciki kadai ba, mai juna biyu yaron ciki, wasu magungunna, emotional stress kamar tsoro, cutar gallbladder, guba a abinci, infection kamar murar ciki, cin abinci dayawa, reaction na doyi, attack na zuciya, rauni a kwalwa, wasu cancers din, ulcer, ciwon suger, shan barasa dasauransu. Abinda yakesa tashin zuciya ko amai ya banbanta a tsakanin shekaru misali ga yara, yazama ruwan dare suyi amai bayan sunsha madara saboda allergy, ulcer, cin abinci mai guba,tari, zazzabi, chunkushewar hanji wanda yake zuwa da zazzabi dayawa. Idan tashin zuciya yana faruwa daga gama cin abinci ko amai yana nuna, alamun ulcer,  abincin da akaci akwai poisoning, bulimia, gastritis. Amma idan yana kaiwa hour daya zuwa takwas bayan gama cin abinci yana nuna guba a abinci, sannan wasu bacteria na cikim abinci na haifarda haka.

Comments

  1. Salamu alaikum zauren kiwon lafiya anyi sallah lfy inada mata a asibiti tayi sati uku yanzu haka amma kullun saitayi amai dasafe anyi allura tsayar da amai amma kullun saitayi shi sungwada suche tanada ulcer ammakuma kullun sai andaura mata ruwa saboda aman datakeyi shine nake neman shawara

    ReplyDelete

Post a Comment